John 11

1To wani mutum mai suna Li’azaru, yayi rashin lafiya. Shi mutumin Baitanya ne, wato kauyen su Maryamu da ‘yar’uwarta Matta. 2Wato wannan Maryamu da ta shafe Ubangiji da mur ta kuma share masa kafafunsa da gashin kanta, wadda dan’uwanta Li’azaru ke rashin lafiya.

3‘Yan’uwannan mata suka aika sako wurin yesu, cewa, “Ubangiji, duba, shi wanda kake kauna yana rashin lafiya”. 4Da Yesu ya ji, sai ya ce “Wannan ciwo ba zai kai ga mutuwa ba, amma domin daukakar Allah ne, domin Dan Allah ya sami daukaka tawurin ta”.

5Yesu yana kaunar Matta, da ‘yar’uwarta da Li’azaru. 6Da yaji cewa Li’azaru na rashin lafiya, sai ya tsaya kwana biyu a inda ya ke. 7Bayan haka, sai ya ce wa almajiransa, “Bari mu je Yahudiya kuma.”

8Sai almajiransa suka ce masa, “Mallam, harwayau Yahudaya na neman ka domin su jefe ka da duwatsu, kuma kana son komawa can?” 9Yesu ya amsa, “Ba sa’a goma sha biyu ce ta haske a rana guda ba? Idan mutum ya yi tafiya da rana, ba za ya yi tuntube ba, domin yana gani ta wurin hasken wannan duniya.

10Amma idan mutum ya yi tafiya chikin dare, za ya yi tuntube domin haske ba ya tare da shi. 11Ya fadi wadannan al’amura, kuma bayan wadannan abubuwa, sai ya ce masu, “Abokinmu Li’azaru ya yi barci, amma zan je don In tashe shi daga barci”.

12Sai almajirai suka ce masa, “Ubangiji, idan barci yake yi, ai za ya farka.” 13Yesu kuwa ya yi maganar mutuwar Li’azaru ne, amma su suna tsammani yana magana akan barci ne na hutu. 14Sai Yesu ya yi masu bayani cewa, “Li’azaru ya mutu.

15Ina farinchiki domin ku, da bani a wurin domin ku gaskata. Bari mu je wurinsa.” 16Toma wanda ake kira Dan tagwaye, ya ce wa sauran almajirai, “Bari mu tafi domin mu mutu tare da Yesu.”

17Da Yesu ya iso, sai ya tarar cewa Li’azaru ya rigaya ya yi kwana hudu a kabari. 18Baitanya kuma tana kusa da Urushalima, ‘yar tafiya marar nisa ce a tsakanin su. 19Yahudawa dayawa sun zo wurin Maryamu da Matta domin su yi masu ta’aziyar mutuwar dan’uwansu. 20Da Matta ta ji cewa Yesu na zuwa, sai ta tafi domin ta same shi, amma Maryamu na zamne a cikin gida.

21Matta ta ce wa Yesu, “Ubangiji, da kana nan tare da mu, da dan’uwana baya mutu ba”. 22Ko yanzu na san cewa duk abinda ka roka a wurin Allah, za ya ba ka. 23Yesu ya ce mata, “Dan’uwanki za ya rayu kuma.

24Sai Matta ta ce masa, “Na san zaya rayu kuma a tashin mattatu na ranar karshe.” 25Yesu ya ce mata, “Ni ne tashin matattu, ni ne kuma rai; wanda ya bada gaskiya gare ni, ko ya mutu, za ya rayu; 26Kuma duk wanda yake raye, ya kuma bada gaskiya gare ni, ba zai mutu ba dadai. Kin gaskata da wannan?”

27Sai ta ce masa, “I, Ubangiji, Na gaskata cewa kaine Almasihu, Dan Allah, wanda ke zuwa duniya. 28Sa’adda ta fadi haka, sai ta koma ta kira yar’uwarta Maryamu gefe guda. Ta ce, “mallam ya iso, kuma yana kiran ki.” 29Da ta ji haka, sai ta tashi da sauri ta tafi wurin sa.

30Yesu bai rigaya ya shiga kauyen ba, yana nan inda Matta ta zo ta same shi. 31Da Yahudawan nan dake tare da Maryamu, wato wadannan da suka zo mata ta’aziya, suka ga ta fita daga chikin gida da sauri, sai suka bi ta, suna tsammanin cewa ta tafi ta yi kuka ne a kabari. 32Da Maryamu ta kai inda Yesu ya ke, sai ta fadi gaban sawayensa, ta ce, “Ubangiji, inda kana tare da mu, da dan’uwana bai mutu ba”.

33Da Yesu ya gan ta tana kuka, da wadannan Yahudawa da suka bi ta, sai ya yi juyayi a ruhu ya damu kuma; 34sai ya ce, “A ina kuka kwantar da shi?” Sai suka ce masa, “Ubangiji, zo ka gani.” 35Yesu ya yi kuka.

36Sai Yahudawa suka ce, “Dubi yadda yake kaunar Li’azaru!” 37Amma wadansun su suka ce, “Shi wannan mutum da ya iya ba makaho ganin gari, da bai iya hana wannan mutum mutuwa ba?

38Yesu yana cikin juyayi kuma a cikin kansa, sai ya tafi kabarin. Kabarin a kogo ne an kuma rufe bakinsa da dutse. 39Sai Yesu ya ce, “A kawar da dutsen.” Matta yar’uwar Li’azaru wanda ya mutu, ta ce wa Yesu, “Ubangiji, Yanzu jikin ya ruba domin ya kai kwana hudu da mutuwa”. 40Yesu ya ce mata, “Ba na ce maki idan kin gaskata za ki ga daukakar Allah ba?”

41Sai suka kawar da dutsen. Yesu ya daga idanunsa ya ce, “Uba, na gode maka domin kana ji na.” 42Na san kana ji na a kowane lokaci, amma domin wannan taro da ke tsaye kewaye da ni nike wannan magana, domin su bada gaskiya cewa kaine ka aiko ni.”

43Bayan ya yi wannan magana, sai ya daga murya ya ce, “Li’azaru, ka fito!” 44Sai mataccen ya fito; kafafunsa da hannayensa na daure da likkafani, fuskarsa kuma na lullube da tsumma. Yesu ya ce masu, “Ku kwance shi, ya tafi”.

45To dayawa daga cikin yahudawan da suka zo wurin Maryamu suka kuma ga abinda Yesu ya yi, suka gaskata da shi; 46amma wadansu suka koma wurin farisawa suka fada masu abubuwan da Yesu ya yi.

47Sai manyan firistoci da farisawa suka tara majalisa wuri guda, suka ce, “menene za mu yi?” Mutumin nan yana alamu masu yawa. 48Idan mun kyale shi haka, duka za su gaskata da shi; Romawa za su zo su kwace wurinmu da al’ummar mu.

49Duk da haka, wani daga cikin su wato, Kayafas wanda shine babban firist a wannan shekara, ya ce da su, “baku san komai ba”. 50Ba ku lura cewa ya fi maku kyau mutum daya ya mutu domin mutane, a maimakon dukan al’umma ta hallaka.”

51Ya fadi wannan ne ba don kansa ba, amma sabo da shine babban firist, ya yi anabci ne cewa ya kamata Yesu ya mutu domin al’ummar; 52kuma ba don alummar kawai ba, amma domin a tattara ‘ya’yan Allah da suke warwatse ko’ina wuri daya. 53Tun daga wannan rana suka fara neman hanyar da za su kashe Yesu.

54Tun daga nan Yesu ya dena tafiya a sarari chikin Yahudawa, amma sai ya koma wani yanki kusa da jeji a wani gari da ake kira Ifraimu. A can kuma ya zamna da almajiransa. 55Idin ketarewa na Yahudawa ya yi kusa, da yawa sun tafi Urushalima daga yankin kasar kamin ranar idi domin su tsarkake kan su.

56Suka shiga neman Yesu, suna magana da junan su yayin da suke tsaitsaye a haikali, cewa “me kuke tunani? Ba za ya zo idin bane?” Babban firist da farisawa sun rigaya sun ba da umurni cewa duk inda aka ga Yesu a zo a shaida domin su kama shi.

57

Copyright information for HauULB